Rundunar ‘ yan Sanda ta Jihar Kaduna, ta ce ‘yan bindiga sun kashe akalla ‘yan banga 17 a kauyen Jan-Ruwa da ke Karamar Hukumar Birnin Gwari ta Jihar Kaduna.
Kakakin rundunar Yakubu Sabo, ya ce jami’an su sun samu rahoton cewa, a ranar 12 Ga Maris da misalin karfe 11:45, wasu mahara sun shiga kauyen Jan-Ruwa sun yi awon gaba da shanu.
Ya ce ana cikin haka sai wani gungun ‘yan sintiri da ke kan hanyar zuwa Jan-Ruwa, su ka samu labari, inda su ka bi barayin cikin daji aka yi barin-wuta har aka kashe ‘yan sintiri da dama.
Kakakin ‘yan sandan ya cigaba da cewa, jami’an ‘yan sanda da su ka hada da na kwantar da tarzoma da ‘yan sintiri sun kai dauki, inda su ka tsinto gawarwaki 15 daga baya kuma an kara samun wasu gawarwaki biyu.
Kwamishinan ‘yan Sanda na jihar Kaduna Ahmad Abdurrahaman ya yi tir da wannan lamari, ya na mai shan alwashin kamo maharan domin su fuskanci hukuncin abin da su ka aikata.