Wata kotu a jihar Gombe, ta yanke wa wani kansila hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni uku sakamakon samun sa da laifin sayen kuri’u.
Hukumar yaki da cin hanci da rashawa EFCC ce ta gurfanar da shi a gaban kotu, bayan ta zarge shi da aikata laifin a lokacin zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisun tarayya da aka yi.
EFCC ta ce ta kama kansilan mai suna Ishiyaku Garba a rumfar zabe mai lamba 007 da ke mazabar Bolari ta jihar Gombe, inda ta rutsa shi ya na raba kudi a rumfar zaben.
Ishiyaku Abubakar dai ya amsa laifin da ake zargin sa da aikatawa, bayan alkalin kotun ya karanto masa jerin laifuffukan da ake zargin sa da su.
A lokacin zaman kotun, lauya mai kare kansilan ya roki kotun ta sassauta wa wanda ake zargin wajen yanke masa hukunci.
Kotun dai ta samu kansilan da laifuffuka uku, inda ta yanke mashi hukuncin zaman gidan yari na tsawon watanni uku ko kuma ya biya tarar naira 295,000.



































