Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa Sanata Abdullahi Adamu,
ya ce zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisun tarayya da ya
gudana ya na cike da naƙasu domin an samu aibi a cikin sa.

Abdullahi Adamu ya bayyana haka ne, yayin da ya ke jawabi
a wajen taron kwamitin gudanarwa na jam’iyyar APC, wanda
zababben shugaban ƙasa Bola Tinubu da mataimakin sa
Kashim Shettima su ka halarta a ɗakin taro na Banquet da ke
Abuja.

Da ya ke jawabi a wajen taron, Abdullahi Adamu ya taya
zaɓaɓɓun ‘yan siyasar murna, amma ya ce zaɓen da ya ayyana
su a matsayin wadanda su ka yi nasara ya na cike da naƙasu.

Ya ce adalci ne su amince cewa zaben ranar 25 ga watan
Fabrairu ba cikakke ba ne, sai dai ya ce a tarihin duniya babu
inda zabe ya gudana cikakke babu naƙasu.

Leave a Reply