Hukumar hana yaduwar cututtuka ta kasa NCDC, ta bayyana cewa wasu mutane 23 sun kamu da Zazzabin Lassa a Nijeriya.

Shugaban hukumar Chikwe Ihekweazu ya sanar da haka, inda ya ce hukumar ta gano haka ne daga jihohi tara, wadanda su ka hada da Edo da Ondo da Ebonyi da Bauchi da Taraba da Imo da Enugu da Benue da kuma  Kebbi.

Ihekweazu, ya ce daga cikin mutanen 23, hudu sun mutu a jihohin Edo da Benue da kuma Bauchi.

Ya ce daga cikin mutane uku din da aka rasa mutum daya ma’aikacin kiwon lafiya ne daga jihar Ebonyi.

Ihekweazu ya kara da cewa, daga watan Janairu zuwa Maris mutane 495 ne su ka kamu da zazzabin Lassa, inda daga cikin su 114 su ka rasa rayukan su a jihohi 21.

Jihohin da cutar ta bulla kuwa sun hada da Edo da Ondo da Bauchi da Nasarawa da Ebonyi da Filato da Taraba da Abuja da Adamawa da Gombe da Kaduna da Kwara da Benue da Rivers da Kogi da Enugu da Imo da Delta da Oyo da Kebbi da Cross River.

Leave a Reply