Shugaban kwamitin yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa Na Jam’iyyar APC gwamna Simon Lalong na Jihar Filato, ya ce ya na farin ciki da jagorancin kwamitin a matsayin shi na Kirista dan darikar Katolika.
Da ya ke zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa da ke Abuja, Simon Lalong ya ce an haife shi kuma ya tashi a matsayin dan darikar Katolika, yayin da ya ke rike da kyauta mafi girma daga ofishin Fafaroma, saboda haka Fafaroma bai shaida ma shi cewa haramun ne jagorancin yakin neman zaben ‘yan takara Musulmi ba.
Gwamna Lalong, ya ce bayan nadin da aka yi ma shi a matsayin jagoran yakin neman zaben, daga cikin wadanda su ka tarbe shi a tashar jiragen sama ta Yakubu Gowon da ke Jos har da wakilan kungiyar Kiristocin Nijeriya.
Lalong ya kuma bayyana shakku game da wadanda ke ikrarin zama Kiristoci da ke adawa da nadin da aka yi masa, yayin da ya yi watsi da wasu shugabannin addinin da ke bukatar ya yi watsi da mukamin saboda abin da su ka kira kin ba Kirista damar samun kujerar wanda zai mara wa Tinubu baya.



































