Janar Abdulrahman Dambazau, Ministan Harkokin Cikin Gida
Janar Abdulrahman Dambazau, Ministan Harkokin Cikin Gida

Hukumar shiga da fice ta kasa ta bada umurnin kulle daukacin iyakokin Nijeriya da ke makwabtaka da sauran kasashe daga karfe 12  na yau Juma’a zuwa 12 na ranar lahadi.

 Kakakin hukumar Sunday James ya bayyana haka a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a madadin shugaban hukumar Muhammad Babandede.

Ya ce gwamnatin tarayya ta bada umurnin kulle dukkanin iyakokin Nijeriya daga karfe 12 na ranar Juma’a zuwa karfe 12 na ranar Lahadi 24 ga watan Febrairun shekara ta 2019.

James ya kara da cewa, an dauki wannan mataki ne domin hana shige da ficen kayayyaki a lokacin  gudanar da zabe, saboda haka ake sanar da al’umma cewa an kulle dukkanin iyakokin Nijeriya da su ka kunshi  Nijar da Chadi, da kuma Kamaru.