Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya karbi rahoton kwamitin bada shawara a kan yadda za a fara biyan sabon karin albashi da majalisa ta amince da shi.

Kwamitin dai, ya mika wa shugaba Buhari rahoton ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Idan dai za a iya tunawa, a ranar 9 watan Janairu ne shugaba Buhari ya kafa kwamitin a karkashin jagorancin masanin tattalin arziki Bismarck Rewane, bayan jaddada aniyar sa ta kara ma fi karancin albashin ma’aikata.

Shugaba Buhari, ya fara bayyana niyyar sa ta yin karin albashin ne a watan Disamba na shekara ta 2018, yayin gabatar da kasafin kudi a gaban ‘yan majalisun dokoki na tarayya.

Ya ce kwamitin zai ba gwamnati shawarwari a kan yadda za ta samu sukunin biyan mafi karancin albashin ba tare da an samu hauhawar farashin kayayyakin masarufi da matsalar rage yawan ma’aikata ba.Sai dai ministan kasafi da tsare-tsare Udo Udoma, ya ce gwamnatin tarayya za ta kara yawan kudin haraji a kan kayan masarufi domin samun kudaden da za ta iya biyan sabon karin albashin.

Leave a Reply